3
 1 Dare farai a kan gadona 
na nemi wanda zuciyata take ƙauna; 
na neme shi amma ban same shi ba. 
 2 Zan tashi yanzu in zagaya gari, 
in ratsa titunansa da dandalinsa; 
zan nemi wanda zuciyata take ƙauna. 
Saboda haka na neme shi, amma ban same shi ba. 
 3 Masu tsaro suka gamu da ni 
yayinda suke kai kawo a cikin birni, sai na ce, 
“Kun ga mini wanda zuciyata take ƙauna?” 
 4 Rabuwata da su ke nan 
sai na sami wanda zuciyata take ƙauna. 
Na riƙe shi, ban yarda yă tafi ba 
sai da na kawo shi gidan mahaifiyata, 
zuwa ɗakin wadda ta yi cikina. 
 5 ’Yan matan Urushalima, ku yi mini alkawari 
da bareyi da ƙishimai na jeji. 
Ba za ku tā da ko ku farka ƙauna ba 
sai haka ya zama lalle. 
 6 Wane ne wannan mai zuwa daga hamada 
kamar tunnuƙewar hayaƙi, 
cike da ƙanshin turaren mur da lubban 
da aka yi da kayan yajin ’yan kasuwa? 
 7 Duba! Abin ɗaukar Solomon ne, 
jarumawa sittin suke rakiya, 
zaɓaɓɓun sojojin Isra’ila, 
 8 dukansu suna saye da takobi 
dukansu ƙwararru ne a yaƙi, 
kowanne da takobinsa a rataye a gefensa, 
a shirye don abubuwan bantsoro na dare. 
 9 Sarki Solomon ya yi wa kansa abin ɗauka; 
ya yi shi da katako daga Lebanon. 
 10 An yi sandunansa da azurfa, 
aka yi ƙasarsa da zinariya. 
An lulluɓe wurin zaman da zanen shunayya, 
’yan matan Urushalima sun yi mata irin yayen da ake yi na ƙauna. 
 11 Fito, ku ’yan matan Sihiyona, 
ku ga Sarki Solomon yana saye da rawani, 
rawanin da mahaifiyarsa ta naɗa masa, 
a ranar aurensa, 
Languages