Zabura 75
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. 
 1 Muna maka godiya, ya Allah, 
muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; 
mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki. 
 2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; 
ni ne wanda yake shari’ar gaskiya. 
 3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, 
ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. 
Sela
  4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ 
ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku. 
 5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; 
kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’ ” 
 6 Ba wani daga gabas ko yamma 
ko hamada da zai ɗaukaka mutum. 
 7 Amma Allah ne mai yin shari’a, 
yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani. 
 8 A hannun Ubangiji  akwai kwaf 
cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; 
yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa 
su sha shi tas. 
 9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; 
zan rera yabo ga Allah na Yaƙub, 
 10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, 
 Languages
Languages