Zabura 63
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. 
 1 Ya Allah, kai ne Allahna, 
da nacewa na neme ka; 
raina yana ƙishinka, 
jikina yana marmarinka, 
cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye 
inda babu ruwa. 
 2 Na gan ka a wuri mai tsarki 
na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka. 
 3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, 
leɓunana za su ɗaukaka ka. 
 4 Zan yabe ka muddin raina, 
kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana. 
 5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; 
da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka. 
 6 A gadona na tuna da kai; 
ina tunaninka dukan dare. 
 7 Domin kai ne mai taimakona, 
ina rera a cikin inuwar fikafikanka. 
 8 Raina ya manne maka; 
hannunka na dama yana riƙe da ni. 
 9 Su da suke neman raina za su hallaka; 
za su gangara zuwa zurfafan duniya. 
 10 Za a bayar da su ga takobi 
su kuma zama abincin karnukan jeji. 
 11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; 
dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, 
 Languages
Languages